MediaOfIslam.Com: Fatwah

Latest

Post Top Ad

Mediaofislam.com
Showing posts with label Fatwah. Show all posts
Showing posts with label Fatwah. Show all posts

Tuesday, January 1, 2019

Hukuncin Sallah Kan Mashayin Giya

January 01, 2019 0
Assalamu Alaikum.
To Allah ya gafarta malam, wanda ya san wajibcin sallah da azumi akansa amma saboda ya taba jin fatawar cewa duk wanda yasha giya sai yayi kwana 40 ba’a ansar ibadar sa shi kuma baya kwana 40 baisha giya ba sai yabar sallah da azumi tsawon shekaru, yanzu kuma ya tuba ya bari ya ramuwar sallar da azumin da yabari zai kasance?
Related image
Wa’alaikumussalam
Amsa
Lallai hadisai sun nuna ba’a karbar sallar wanda ya sha giya ta kwana arba’in kamar yadda yazo cikin silsilah swahiha 709, hadisin ya nuna idan mutun ya tuba Allah zai yafe masa, saboda haka tunda ya tuba muna fatar Allah zai yafe masa, sai yaci gaba da istigfari da yawaita ibada,
Malamai sunyi sabani wajen ramakon sallah da azumi ga wanda yabar su baiyi har tsawo wani lokaci,  wasu sunce zai rama wannan shine ra’ayin Jamhurun malamai  waau kuma sunce ba zai rama ba don sun gina fahimtar su akan dalilai na shari’a da suka nuna kafurcin wanda yabar sallah, sannan suka ce in ance zai ya rama hakan ka iya wahalar dashi kila ya kasa ya koma gidan jiya,  suna hujja kuma da fadar cikin Suratul Ɗaha 11, da ta 82.
Don haka dai babu ramuwa akan sa sai istigfari da tsaida sallah da ci gaba da azumi da lazimtar ibada sosai da sosai, an tambayi malaman  lajna 6/41 hukuncin wanda yabar sallah da azumi sun bada fatawar ba zai rama ba.
Wallahu A’alam.
Malam Nuruddeen Muhammad Mujaheed
07/08/2016.
Daga : ZAUREN FIQHUS SUNNAH group.
Read More

Yadda Ake Yin Sallar Jana’iza

January 01, 2019 0
YAN-UWA Mafi yawancinmu, muna yin Sallar Jana’iza amma kuma ba mu san abinda ake fada a cikin kowacce Kabbara ba. Dan hak shi yasa na ga cewa yana da kyau in ware mana wani lokaci na musamman, Domin in fahimtar
da mu yadda ake yin sallar Jana’za.

Image result for sallar gawa
‘YAN-UWA ita dai Sallar janai’za, tana da babban lada, ga wanda ya aikata
ta kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya koyar, dan haka yana da kyau, mu tsaya mu koya.
Kamar yadda na ce, sallar jana’za tana da kabbarori guda hudu ne
kawai kuma kowacce Kabbara da abin da ake fada a cikinta.
1. KABBARA TA FARKO ana karanta {suraul-fatiha} ne kawai, banda wata sura, ko wata a’ya.
2. KABBARA TA BIYU ana karanta Salatin Annabi ba wani salati na daban ba.
3. KABBARA TA UKU ana yin addu’a ga wanda ya mutu mace ko namiji.
4. KABBARA TA HUDU za ka yi addu’a ne a kanka da sauran al’ummar Musulmi.
DAN UWA KANA GAMAWA sai ka jira Liman ya yi sallama. Ita kuma sallamar guda daya ce tak! Kuma za ka yi ta ne a bangaren damanka.
Allah muke roko da ya kara tabbatar damu akan Sunnar Annabin Rahama, Manzon Allah (S.A.W).
Akwai bukatar a yada domin ‘yan uwa musulmai su karu.
source@http://fiqhussunnah.blogspot.com
Read More

Post Top Ad

Mediaofislam.com